mahaifinane ke lalata dani har na dauki ciki—A cewar Hafsat
Kamar yadda kuka sani a addinance ko al’adance iyaye ne ya kamata su kula ko su lura su sanya idanu a kan tarbiyyar ya’yanzu to sai dai kash abin ba haka yake ba ga malam Audu wanda shi a nashi bangare shine da kansa ya ke yin lalata da diyar cikinsa.
Wanda har hakan ya jawo ta dauki juna biyu wato yayi mata cikin shege, da take zantawa da manema labarai diyar mai suna Hafsat Audu ta bayyana wa manema labarai cewa.
“Ni mahaifiyata ya sake ta ta bar gidan kuma kullum da daddare da zarar ya dawo sai ya kira ni zuwa dakinsa bayan na je sai ya rufe kofa yace in tube kayana in kwanta ni kuma sai in yi saboda idan nayi masa gardama dukana yake yi kuma har cewa yake zai tsine min in bar duniya”
Kamar yadda ta shaidawa manema labarai, wannan lamari dai ya faru ne a jihar Taraba, dake yankin arewacin Najeriya, idan baku manta ba kona shekarar da ta gabata ta 2020 saida aka samu rahoton faruwar makamancin wannan labari.
Inda a can din ma wani magidanci ya yi lalata da diyar cikinsa, muna fatan Allah ya kiyaye mu daga mummunar kaddara ameen.
Kada kumanta kudanna mana Alamar kararrawar sanarwa domin samun jin kararrawar sanarwar shirye-shiryenmu Masu ƙayatar wa mungode.