Mawaƙi SS Danko zai zama ‘mai igiya biyu’ Juma’a mai zuwa

0

Mawaƙi SS Danko zai zama ‘mai igiya biyu’ Juma’a mai zuwa - Kannywood - News, reviews and more › hausa

Ibrahim SS Danko da Nusaiba Shu’aibu za su zama ɗaya nan da kwana biyu

MAWAƘIN siyasa a Kannywood, Ibrahim Shehu Suleiman, wanda aka fi sani da SS Danko, shi ma ya yunƙoro zai ƙara aure kafin shekarar nan ta ƙare, domin kuwa yau saura kwana biyu ya zama mai igiya biyu.

Za a ɗaura auren SS Danko da sahibar sa, Nusaiba Shu’aibu, a ranar Juma’a, 23 ga Disamba, 2022.

Related Posts
1 of 405

Ibrahim SS Danko

Katin ɗaurin auren, wanda mujallar Fim ta samu, ya nuna cewa za a ɗaura auren da misalin ƙarfe 2:30 na rana a Ƙofar Gayan, daura da Kogoro, Zone II, lamba 17, Abbas Street, Zariya, Jihar Kaduna.

Wakilin mu ya ruwaito cewa SS Danko ya yi auren sa na farko a Mayun shekarar 2018.

Haka kuma shi ne babban mawaƙin ɗan takarar zama sanatan Kano ta tsakiya, A.A. Zaura.

Katin ɗaurin auren Ibrahim da Nusaiba

Leave A Reply

Your email address will not be published.

This website uses cookies to improve your experience. We'll assume you're ok with this, but you can opt-out if you wish. Accept Read More

Privacy & Cookies Policy